Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Obasa Ya Bayyana A Majalisar Dokokin Legas


Mudashiru Obasa
Mudashiru Obasa

A wani mataki na nuna goyon baya, masoyansa sun taru a kofar shiga ginin majalisar, sun rera wakoki da jinjina ga dan majalisar mai wakiltar mazabar Agege a majalisar

Yayin da ake tsaka da rikicin shugabancin daya tarwatsa zaman lafiyar da ake da shi a Majalisar Dokokin jihar Legas, hambararren kakakinta, Mudashiru Obasa, ya bayyana a zauren majalisar a yau Alhamis.

Obasa ya samu rakiyar wata tawagar jami’an tsaro masu sanye da kayan sarki kuma dauke da makamai cikin murtakakkiyar fuska sa’ilin daya shiga zauren majalisar wanda rabon da a ganshi a bainar jama’a tun bayan da aka sauke shi daga kan kujerarsa a ranar Litinin, 13 ga watan Janairun 2025.

A wani mataki na nuna goyon baya, masoyansa sun taru a kofar shiga ginin majalisar, sun rera wakoki da jinjina ga dan majalisar mai wakiltar mazabar Agege a majalisar mai mambobi 40.

Idan muka yi waiwaye zuwa watan Janairu, an tsige obasa daga kan kujerar shugabancin majalisar dokokin Legas da rinjayen kaso 2 bisa 3 na kuri’un da aka kada bisa zarginsa da rashin da’a da laifuffuka daban-daban.

Nan take aka maye gurbin Obasa da, mataimakiyarsa ta wancan lokaci, Mojisola Meranda, a matsayin sabuwar kakakin majalisar, abinda ya mayar da ita mace ta farko data taba shugabantar Majalisar Dokokin jihar dake shiyar kudu maso yammacin Najeriya.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG