Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yi Hasarar Rayuka A Jihar Nassarawa


Hanyar zuwa Lafia daga cikin garin Akwanga, Jihar Nassarawa, a bayan rikicin da ya faru a Alakyo. Matan 'yan sandan da aka kashe sun tare hanyar, su na jimamin mazajensu da aka kashe, abinda ya haddasa cunkoson ababen hawa.
Hanyar zuwa Lafia daga cikin garin Akwanga, Jihar Nassarawa, a bayan rikicin da ya faru a Alakyo. Matan 'yan sandan da aka kashe sun tare hanyar, su na jimamin mazajensu da aka kashe, abinda ya haddasa cunkoson ababen hawa.

An kashe 'yan sanda da dama a lokacin da suka yi yunkurin kamo madugun wata bkungiyar asiri da ake kira Ombatse

Wani rikici da ya barke a garin Alakyo dake karamar hukumar Lafiya a jihar Nassarawa ya yi sanadin rasa rayukan mutane da dama, akasarinsu 'yan sanda.

Wannan al'amari ya faru a lokacin da 'ya'yan kungiyar asiri ta Ombatse, ta 'yan kabilar Eggon, suka yi kwanton bauna suka far ma 'yan sandan da suka je neman kama madugun wannan kungiya, bisa zargin cewa yana tara makamai tare da haddasa fada a yankin.

Tuni gwamnan jihar, Tanko Almakura,ta sanar da fadar shugaban kasa dangane da lamarin wanda tun farko ya haramta kungiyar sabili da cin zarafi da tursasawa al’umma da ake zarginta da yi.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:05 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG