Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ministoci: Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Ya Karanta Sunayen Da Za A Tantance


Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki
Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki

Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana sunayen da Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar ma ta don tantancewa.

Yau ne Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Abubakar Bukola Saraki ya karanta sunayen Ministocin da Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ma Majalisar don tantancewa. Wakiliyarmu a Abuja Madina Dauda ta ruwaito Shugaban Majalisar Dattawan na cewa karanta sunayen Ministocin, wadanda su ka hada da: Abubakar Malami, daga jahar Kebbi; da Janar Abdurrahman Bello Danbazau daga jahar Kano; da Aisha Jummai Alhassan, daga jahar Taraba; da Alhaji Laye Muhammed; da Babatunde Raji Fashola daga jahar Lagos; da Barrister Adebayo Shittu; da Barrister Solomon Dalong, daga jahar Filato.

Sauran mutanen da aka gabatar da sunayensu don tantancewar sun hada da Sanata Chris Ngige daga jahar Anambra; da Rotimi Amaechi, jahar Rivers; da Chief Audu Innocent Ogbeh, daga jahar Kogi; da Mrs Amina Ibrahim; da Dr. Osage ENARE da Dr Emanuel Ebe Kachukwu da Dr Kayode Fayemi , jahar Ekoiti; da Injiniya Suleiman Adamu da Mrs Kemi Adiosun; da Dr. Ogbunaya Onu, jahar Abia; da Ahmed Isa Ibeto, daga jahar Nasarawa; da Ibrahim Usman Jibrin da Sanata Hadi Sirika, daga jahar Katsina; da Sanata Udoma Udo Udoma, daga jahar Akwa-Ibom.

Tuni dai aka fara cece-kuce kan sunayen. Wani Sanata dan jam’iyyar PDP y ace da sun yi tsammanin za a gabatar da sunayen wasu sabbin mutane ne, to amma sai gashi mutanen da su ka sani ne. Hasalima, in ji shi, wasunsu sun yi aiki tare. Y ace duk da haka za su gayyaci hukumomin ICPC da EFCC su binciki kowannensu.

Shi kuwa wani dan jam’iyyar APC Sanata Mohammed Shaba Lafiagi y ace za a bi tsarin da aka saba bi ne wajen tantancewar.

Madina ta ce ranar Talata mai zuwa 13 ga wata ne za a yi tantancewar.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:14 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG