Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matar Gwamnan Jahar Borno Ta Bayyana Dalilanta Na Kafa Gidauniyar Taimakon Gajiyayyu


Wasu matan da aka ceto daga hannun Boko Haram
Wasu matan da aka ceto daga hannun Boko Haram

Yayin da ake ta kiraye-kirayen a taimaka ma masu fama a jahar Baorno, matar gawamnan jahar ta bayyana cewa ta kai dauki ma mabukata ne saboda ganin irin halin da su ke ciki na ban tausayi.

Matar gwamnan jahar Borno, Hajiya Nana Kashim Shattima ta ce ta kafa gidauniyar tallafa ma ,marayu da sauran marasa galihu ne saboda ta lura cewa a matsayinta na matar gwamna wani sa’in ta kan yi fama da rashi balle matan marasa galihu da sauran mabukata.

Ta take amsa tambayoyi, Hajiya Nana Shattima ta yi kira ga sauran kungiyoyi masu zaman kansu da kea din kasar da su bi sahu wajen tallafa ma dinbin mata da marayu da sauran marasa karfi da ke jahar, wadanda rikicin ‘yan tada kayar baya ya shafe su.

Ta ce kodayake kungiyoyin na kokari sosai, to amma dole ne su kuma da ke tare da jama’a su cigaba da kiraye-kirayen a kara azama wajen bayar da taimakon. Ta gode ma kungiyoyin da ke taimaka ma mata masu fama da cutar yoyon fitsari.

Ga Haruna Dauda da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:07:37 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG