Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manchester City Za Ta kara Da Copenhagen


Champions League
Champions League

Za a fara wasannin farko a watan Fabrairu sannan a buga zagaye na biyu a Maris din 2024.

Manchester City, wadda a bara ta yi nasarar lashe kofin zakarun nahiyar turai, za ta kara da FC Copenhagen a zagaye na biyu na gasar a bana, bayan an shirya jadawalin zagaye na biyu yau, Litinin 18 ga watan Disamba.

A sauran wasanni da za a kara a zagayen na biyu, Arsenal wadda ta ja rukuni na biyu za ta fafata da FC Porto da ta kare na biyu a rukuninta da Barcelona ta jagoranta.

Ita Barcelona za ta kara da kulob din Victor Osimhen wanda ya lashe kyautar gwarzon dan wasan gasar CAF, Napoli. Bayern Munich na kasar Jamus za ta yi gurmuzu da Lazio, sai kuma RB Leipzig ta kasar Jamus wadda za ta karbi bakoncin Real Madrid ta kasar Spaniya a filin wasanta na Red Bull Arena.

Haka kuma Atletico Madrid za ta marabci Inter Milan a filin Metropolitano.

Za a fara wasannin farko a watan Fabrairu sannan a buga zagaye na biyu a Maris din 2024.

Za a buga wasan karshe na gasar zakarun turai ta bana a filin wasa na Wembley da ke Landan a ranar 1 ga watan Yuni.

Ga cikakkiyar jadawalin Gasar Zakarun Nahiyan Turai zagaye na biyu

  • Porto da Arsenal
  • Napoli da Barcelona
  • PSG da Real Sociedad
  • Inter Milan da Atletico Madrid
  • PSV Eindhoven da Borussia Dortmund
  • Lazio da Bayern Munich
  • Copenhagen da Manchester City
  • RB Leipzig da Real Madrid

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG