Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za A Dawo Da Buga Kwallon Kafa na Kasa Da Kasa A Somalia A Shekara Mai Zuwa


Jami'an kwallon kafa na Somaliya
Jami'an kwallon kafa na Somaliya

Hukumar kwallon kafa ta Somaliya na ganin cewa idan ta dauki nauyin wasan kwallon kafa na kasa da kasa zai taimaka wajen bunkasa tsaron kasar tata.

Hukumar kwallon kafa ta kasar Somalia ta bayyana cewa tana shirin daukar dawainiyar wasan kwallon kafa na kasa da kasa a cikin shekara mai kamawa domin a samu ci gaba a harkokin tsaron kasar.

Shugaban hukumar kwallon kafa na kasar ne Abdqiani Said Arab yace lokaci yayi da kasar ta Somalia zata shirya wasanni kwallon kafa a babban filin wasan dake cikin kasar a shekara mai kamawa.

A cikin sanarwa dake dauke da sa hannun sa yace samun ingaci a harkokin tsaro a kasar, yasa suka yanke shawarar gudanar da wasannin cikin gida.

Yace mutanen kasar ta Somalia suna da damar kallon babban kungiyar wasan kwallon kafa ta kasar suna wasa a cikin gida, don haka yanzu lokaci yayi da zasu gudanar da hakan musammam ma ganin yadda kasar ke kara samun ci gaba.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG