Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Jamus Ta Tallafawa Kananan Hukumomi Hudu a Jamhuriyar Nijar


Shugaban Nijar Issoufou Mahammadou da Shugabar Jamus Angela Merkel
Shugaban Nijar Issoufou Mahammadou da Shugabar Jamus Angela Merkel

Kasar Jamus da wasu kasashen nahiyar turai sun tallafawa kananan hukumomi hudu a Jamhuriyar Nijar da zummar dakile kwararar matasa zuwa kasashen turai

Kananan hukumomi hudu na Junhuriyar Nijar ne kasar Jamus, a karkashin ma’aikatar harkokin wajen kasar, da wasu kasashen turai, suka tallafawa da zummar hana matasa yukurin ratsawa ta kasar Libya zuwa kasashen turai.

Mukhtari Usman, shugaban hukumar mashawarta ta jihar Damagaran, ya yi godiya tare da fatar tallafin zai taimaka wajen kawo ci gaban yankunan nasu.

Kayan da aka raba wa kananan hukumomin sun hada da mashina hudu, da kwamfutoci da wasu kayan aiki. Ana kyautata zaton kayan zasu taimaka wa matasan zama gida maimakon tafiya tafi cirani a wasu kasashen ketare.

Shima Sani Usman, Magajin Garin karamar hukumar Kurmi, daya daga cikin kananan hukumomin da suka ci gajiyar tallafin, yayi fatar tallafin zai taimaka wajen hana matasansu tafiya cirani.

Ga rahoton Tamar Abari da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:37 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG