Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Japan Da Koriya ta Arewa Zasu Cigaba Da Sulhu

​Kasar Japan tace Koriya ta Arewa ta amince a cigaba da bincike akan mutanen Japan da Koriya ta Arewa ta sace a shekarun 1970 da 1980.

Firayim minister Shinzo Abe, ya yabawa wannan mataki Alhamis dinnan a matsayin yunkuri na farko wajen kawo karshin lamarin da ya lalata dangantakar Koriya ta Arewa da Japan.

A 2002 ne Koriya ta Kudu ta amince cewa ta sace mutanen Japan su 13 domin su koyawa masu binciken sirrin kasar al-adun Japan.

An mayarda mutum 5 Japan, kuma Koriya ta Arewan tace ragowar duk sun mutu, amma mutane da yawa a Japan na zargin cewa an kara sace wasu su goma sha wani abu.

Wannan mataki na cigaba da binciken, ya zone bayan share kwanaki 3 ana muhimmiyar tattaunawa tsakanin Koriya ta Arewa da Japan a cikin wannan mako a kasar Sweden.

Da yake mayarda da martani, Sakataren Gwamnatin Japan Yoshi-hide Suga yace kasarshi zata sassauta takunkuman da ta sakawa Koriya ta Arewa, idan aka samu cigaba akan batun mutan Japan din da aka sace.
This item is part of
XS
SM
MD
LG