Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumomin Alhazan Najeriya Su Na Damarar Hawan Arafat


Musulmi su na addu'a a lokacin hawan Arafat
Musulmi su na addu'a a lokacin hawan Arafat

An yi tsarin jigilar alhaza zuwa Mina da Arafat daki-daki domin kaucewa cunkoso, kuma da karfe 12 na daren lahadi za a fara jigilar na Najeriya

Shugabannin alhazan Najeriya da suke gudanar da aikin Hajjin bana a kasa Mai Tsarki, sun bayyana gamsuwa kan yadda aka kammala aikin jigilar alhazai, aka kuma himmatu a yanzu ga gudanar da aikin Hajjin.

Amirul Hajj na Najeriya kuma Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Elkanemi, shi ya bayyana wannan a wurin wani taron da shugabanni da dukkan masu ruwa da tsaki a ayyukan Hajjin na bana suka shirya a Jeddah.

Shi kuma shugaban hukumar alhazai ta Najeriya, Alhaji Musa Bello, yace za su mayarda hankalinsu bana kan batun tsabta a tantunan Mina da Arafat, domin kawar da irin abubuwan da ake gani na rashin tsabta. Yace za a tabbatar da samun hanyar wucewar ruwan alwala ko kwashe tarkaccen abinci daga tantunan alhazan.

Za a kafa kwamitin tsabtan da zai kula da hakan.

Haka kuma hukumomin Sa'udiyya sun tsara kwasar alhazai daki-daki zuwa Mina da Arafat domin kaucewa cunkoso. Za a kwashi alhazan Najeriya zuwa wadannan wurare biyu daga karfe 12 na daren lahadi.

Wakilinmu Mustapha Nasiru Batsari, ya aiko da karin bayani daga Makkah.

Amirul Hajj Da Shugabannin Mahajjatan Najeriya Su Na Kimtsa Alhazai Don hawan Arafat - 2:54
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:54 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG