Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar FIFA Ta Bayyana Cewar Kasashe 48 Zasu Kara A 2022


Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA Gianni Infantino ya ce a shekarar 2022 kasashe 48 ne za su halarci gasar cin kofin duniya, wacce za a yi a kasar Qatar dake daular larabawa.

A da dai an shirya fara amfani da tsarin kasashe 48 ne a shekarar 2026, inda kasashen Amurka, Canada da kuma Mexico za su karbi bakuncin gasar.

Kasashe 32 ne suke halartar gasar ta cin kofin duniya inda a bana aka yi a kasar Rasha wace kasar Faransa ta lashe wasan.

Wannan sauyin zai tilasta wa Qatar ta nema hadin gwiwa da wasu kasashe a yankin Gabas ta Tsakiya, don karbar bakuncin gasar, a cewar shugaban hukumar ta FIFA.

Muna duba yiwuwar hakan, muna tattaunawa da abokanmu a Qatar da sauran kawayenmu da ke yankin, kuma muna fatan hakan mai yiwuwa ne.

Shugaban na FIFA Gianni Infantino, yayi wannan bayanin ne a lokacin da yake jawabi a babban taron hukumar kwallo kafa ta Nahiyar Asiya, a sabuwar shelkwatar hukumar dake Birnin Kuala Lumpur a kasar Malaysia.

Inda ya kara da cewar, ya kamata abai wa kowace kasa damar
fafatawa a gasar cin kofin duniya.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG