Fulani Mata sun maida martani kan kokarin da kungiyar makiyaya a jihar Naija ke yi na hana su tallar nono biyo bayan zargin da ake yi cewa, wadansu matan na fakewa da sana'ar suna badala. Kamar yadda muka alkawarta,
Duk da yake matan sun dorawa wadansu bara gurbi tsakaninsu alhakin wannan maatsalar, sun ce maza ma suna da laifi kasancewa da dama basu kulawa da iyalinsu yadda ya kamata, abinda yake sa da dama fita su nemi abinda zasu ci da 'ya'yansu da biyan sauran bukatun gida.
Saurari cikakken shirin
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.