Idan kuna biye damu, Shirin Domin Iyali ya nemi sanin abinda yafi tsonewa al’umma ido da kuma inda suke butakar gani gwamnati ta bada karfi a wannan shekara da ta kama. Daga cikin wadanda shirin ya yi hira dasu makon jiya, akwai Dr Mohammed Hadi Musa wani mai sharhi kan harkokin iyali da kuma Hauwa Ibrahim El-yakub darekta a wata cibiyar bunkasa karkokin izimi mai zaman kanta a birnin Kano. Ga ci gaban bayanin Hajiya Hawa a hirarsu da wakilinmu Mahmud Ibrahim Kwari.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.