Al’ummar garin Shinfida na jihar Katsina sun shiga halin ni'yasu sakamakon garkuwa da iyalansu da 'yan bindiga suka yi bayanda suka yiwa wani ayarin motoci dake kan hanyar cin kasuwa kwantan bauna suka sha karfin jami’an tsaro daga nan suka tasa keyar matan da aka bari a mota. Shirin Domin iyali ya zanta da wadansu da wannan lamarin ya shafa wadanda kuma zamu saya sunayensu bisa dalilan tsaro.
Saurari cikakken bayanan magidantan da aka yi garkuwa da iyalansu da kuma hirar da shirin ya yi da daya daga cikin matan da aka yi garkuwa da su.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.