A ranar Juma’ar Makon jiya ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi yafiya da afuwa ga wata matashiya, mai suna Rahma Hussaini dake Unguwar Brigade a Kano, wadda babbar kotun Kano ta yankewa hukunci kisa a shekara ta 2014 bayan samun ta da laifin kashe mijinta ta hanyar soka masa wuka a cikin sa.
Matakin gwamnan ya biyo bayan amincewa da shawarwarin kwamitin shugaban kasa kan yiwa daurarru afuwa, da kuma hukumomin kula da gidajen gyaran hali na Kano. Abinda shirin ya maida hankali a kai ke nan wannan makon.
Saurari cikakken shirin:
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.