Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dalilin Da Ya Sa Ban Halarci Babban Taron Kungiyar Lauyoyin Najeriya Ba – Kwankwaso


Presidential candidate of the New Nigeria Peoples Party, NNPP, Rabiu Kwankwaso
Presidential candidate of the New Nigeria Peoples Party, NNPP, Rabiu Kwankwaso

Cikin wasikar, Kwankwaso har ila yau ya ce, abokin takararsa Bishop Isaac Idahosa ya fita kasar waje, “amma da na turo shi don ya wakilce ni.”

Dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar NNPP a Najeriya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce bai amsa gayyatar da kungiyar lauyoyin Najeriya ta yi masa ba ne saboda wasu muhimman ayyuka da suka sha gabansa.

Cikin wata wasika da ya rubutawa kungiyar lauyoyin ta NBA, wacce kakakinsa Abdulmumin Jibril ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya bai wa kungiyar hakuri bisa rashin samun damar halartar taron.

“Ina so na bayyana cewa na samu wasikar gayyatarku, mai dauke da maudi’in da ya gabata, ina kuma so na sanar da ku cewa ba zan samu damar halartar wannan taro mai muhimmanci ba, saboda wasu muhimman abubuwa da ke gabana da suka shafi kasa.” Kwankwaso ya ce cikin wasikar.

Cikin wasikar, Kwankwaso har ila yau ya ce, abokin takararsa Bishop Isaac Idahosa ya fita kasar waje, “amma da na turo shi don ya wakilce ni.”

A ranar Litinin kungiyar ta NBA ta bude babban taronta na kasa a karo na 62 a jihar Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya.

Taron ya samu halartar dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar da dan takarar jam’iyyar LP, Peter Obi.

Kamar Kwankwaso, shi ma dan takarar jam’iyya mai mulki ta APC, Bola Ahmed Tinubu, bai samu halatar taron ba, amma ya tura abokin takararsa Kashim Shettima don ya wakilce shi.

Ire-iren wadannan taruka kan gayyaci ‘yan takarar mukamin shugaban kasa don su kyankyasawa jama’a manufofinsu kan yadda za su tunkari matsalolin kasa.

XS
SM
MD
LG