Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID19: 'Yan Sanda Sun Tarwatsa Mutanen Da Suka Ki Zama Gida


Yadda jami'an tsaro suka harba hayaki mai sa hawaye kan wasu masu zanga-zanga a watannin baya.
Yadda jami'an tsaro suka harba hayaki mai sa hawaye kan wasu masu zanga-zanga a watannin baya.

Yan sandan kwantar da tarzoma a birnin Kisumu na kasar Kenya sun harba barkonan tsohuwa cikin kasuwa da ke cike da mutane, a kokarin tarwatsa mutane saboda dokar da gwamnati ta kafa don dakile yaduwar cutar Coronavirus.

Masu saye da sayarwa a kasuwar, cikin fushi, sun fada wa manema labarai cewa, suna sane da barazanar coronavirus, amma sun ce yawancin ‘yan kasar Kenya matalauta ne, suna bukatar su yi aiki domin samun abinci.

Suka ce idan har gwamnati tana son su zauna a gida, to dole ta basu kudaden da za su iya yin hakan.

Ya zuwa jiya Laraba, kasar Kenya tana da mutane 25 da aka tabbatar da sun kamu da Covid-19.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG