Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID-19: Hannun Agogo Ya Koma Baya a Pakistan


Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta yi kira ga kasar Pakistan da ta sake daukar matakan killacewa, ganin yadda adadin masu kamuwa da cutar corona ya yi matukar karuwa cikin kwanaki da dama.

A wata wasikar da ya tura ma Ma’aikatar Lafiya ta Punjab, jaha mafi gairma a kasar ta Pakistan, wakilin hukumar ta WHO Palitha Mahipala, ya ba da shawarar da a yi amfani da tsarin killacewar nan na sati biyu, sannan kuma a dada kara yawan wadanda ake wa gwajin cutar zuwa 50,000 a rana.

Wannan kasar dai ta samu masu dauke da cutar wajen 113,702, wadanda su ka mutu kuma sama da 2,100, ciki har da mutane 105 da su ka mutu jiya Talata kawai.

Mahipala ya ce adadin masu dauke da cutar ya karu ne tun bayan da larduna da dama suka sake bude harkokin hada-hada a farkon watan Mayu.

Facebook Forum

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG