Al-Ameen Abubakar Ismat, matashi da yake gudanar da karatun shi a matakin digiri na biyu a jami'ar Coventry dake kasar Burtaniya, wanda yake ganin cewar akwai hanyoyi da suka kamata matasa su bi don cin gajiyar kuruciyar su.
Matshin ya gudanar da karatun shi a matakin Firamari da Sakandire a Najeriya, wanda daga bisani ya fita kasar waje don gudanar karatunsa a matakin digirin farko har zuwa na biyu a kasar Ingila.
Haka kuma ya bayyana cewa a duk lokacin da matashi ko matashiya suka tashi tsaye wajen neman ilimi, da tunanin yadda zasu bada tasu gudunmawa wajen cigaban al'uma, lallai babu shakka zasu samu nasara.
Don cigaban wannan tattaunawar sai a biyo mu.
-
Yusuf Harande
Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.