Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Asusun Yaki Da Cututuka Na Duniya Ya Bada Gudummuwa Domin Yaki Da Kanjamau A Najeriya


Wani yana gwada jinin masu fama da cutar kanjamau
Wani yana gwada jinin masu fama da cutar kanjamau
Asusun tallafawa yaki da cututuka na duniya-Global Fund ya bada tallafin dala miliyan biyu da dubu dari biyar domin yaki da cutar kanjamau a jihohi goma sha biyu na Najeriya da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Asusun ya bada tallafin ne musamman domin ceton rayukan jarirai ta wajen hana yada cutar daga uwa zuwa jariri.

Bincike na nuni da cewa, kashi saba’in cikin dari na jarirai sama da dubu biyu da aka Haifa da kwayar cutar kanjamau daga Najeriya suke. Abinda ke nuni da cewa mata masu ciki dake dauke da cutar kanjamau basu samun magani da suke bukata.

Darekta janar na hukumar yaki da cutar kanjamau a Najeriya Farfesa John Idoko yace kashi talatin bisa dari na matsalar yaki da cutar kanjamau yana Najeriya, yace kasashe da suka ci gaba sun daina samun jarirai da suke daukar cutar kanjamau daga iyayensu amma har yanzu ana fama da matsalar a Najeriya.

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG