Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Takawa Masu Zanga Zanga Birki a Congo


NIGER: Zanga zanga a Yamai
NIGER: Zanga zanga a Yamai

Domin takawa masu zanga-zanga a Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo birki, jami'an tsaro sun yi amfani da hayaki mai sa kwalla domin tarwatsa masu boren.

Jami'an tsaron Jamhuriyar Demokaradiyyar Congo sun harba hayakin nan maisa kwalla a coci katolika dake birnin Kinshasa babban birnin kasar.

Sun yi haka ne da niyyar ganin sun hana su gudanar da wata zanga-zangar da aka shirya.

Masu zanga-zanga sun yi dafifi yau Lahadi a harabar cocin domin yunkurin gudanar da zanga-zangan nuna kin jinin shugaba Joseph Kabila.

Kasar ta Jamhuriyar Dimukaradiyyar Congo ta shiga rudunin siyasa ne tun lokacin da shugaba Kabila ya ki sauka akan karagar mulki.

Shugaban wanda a bisa tsari dokar kasar ya kammala wa'adin mulkinsa ne tun a cikin watan Disamban bara.

A lokacin ne ya kamata a ce kasar ta gudanar da wani sabon zaben shugaban kasa a cikin shekarar 2017, wanda hakan kuma ya kasa samuwa.

Wannan kememen da shugaban ya yi tare da jingine batun zabe ya kara harzuka ‘yan kasar ta Jamhuriyar Dimukaradiyyar Congo.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG