Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sance Dalibai 78 A Bamenda Dake Arewacin Kamaru


Ana ta jimamin sace wasu dalibai 78 tare da shugaban makarantar tasu a yankin masu fafutukar 'yan aware na arewa maso yammacin Kamaru masu magana da harshen inglishi.

Yau litinin wasu ‘yan bindiga da ba’a san ko su waye ba, sun yi garkuwa da wasu dalibai 78, da kuma shugaban makarantar Cocin Presbyterian da ke yankin ‘yan aware masu magana da harshen inglishi, a arewa maso yammacin Kasar Kamaru.

Gwamna Deben Tchoffo ya tabbatar da sace daliban 78, da kuma shugaban makarantar da ke kauyen Nkwen a Bamenda, wanda shine babban birnin yankin masu fafutukar ta ‘yan aware masu magana da harshen Inglishi.

Sai dai bayanai sun yi nuni da cewa, ba’a san wadanda suka yi garkuwa da daliban ba, kuma babu masaniya kan dalilin da ya sa suka yi garkuwa da su.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG