Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An kira a kafa kotun da zai hukumta laifin cin zarafin mutane a Sudan ta Kudu


Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir
Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir

Kungiyar dake kare hakin bil Adam ta kira kungiyar tarayyar kasashen Afirka da ta kafa kotu na musamman da zai hukunta duk wadanda suke cin zarafin mutane a Sudan ta Kudu

Kungiyar Human Rights Watch da ke kare hakkin bil adama, ta yi kira ga kungiyar tarayyar kasashen Afrika ta AU, da ta kafa wata kotu wacce za ta hukunta duk wanda aka samu da aikata manyan laifukan cin zarafin bil adama a Sudan ta Kudu.

Kungiyar ta Human Rights Watch ta na zargin bangarorin ‘yan tawayen ne da kuma dakarun gwamnati da aikata laifukan da suka take hakkin bil adama.

A yau Litinin kungiyar ta yi ikrarin cewa akwai hujjojin da ke nuna dakarun kasar sun kashe mutane tare da aikata fyade da kuma tilastawa mutane tserewa daga gaidajensu a jihar Kudancin Equatoria.

A watan da ya gabata, Mataimakin babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ivan Simanovovic, ya bayyana jihar Kudancin Equatoria a matsayin daya daga sabbin yankunan da ake samun tarzoma, inda ya ce sun samu rahoton ana yin kisa da fyade da kuma barnata dukiyoyin jama’a.

XS
SM
MD
LG