Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kame Wasu ‘yan Adawa A Jamhuriyar Kamaru


Shugaban Kamaru, Paul Biya
Shugaban Kamaru, Paul Biya

Tun makon data gabata ne ‘yan adawan suka lashi takobin cewa a duk jumaa zasu yi zanga-zanga ta lumana.

Kuma a duk ranar da zasu yi zanga-zangar zasu sanya bakake kaya, ranar da suka kira ta bakar jumaa.

A ranar Jumaan data gabata a unguwar da ake kira akasiwa dake a birnin Yaounde, ‘yan adawan kusan su goma da suka hada da Kawala shugaban jamiyyar Cameroon Peoples Party da wasu tawagar’yan adawan aka kama su yayin da suke kokarin raba takardu wannan zanga-zangar.

Bayan an kama su ne aka tafi dasu barikin sojan kasar,

Ga Muhammadu Danda da ci gaban rahoton 1’17

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:17 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG