Wata kungiyar hadin kan Musulmi da Kirista a arewacin Najeriya ta kaiwa Sheikh Dahiru Bauchi ziyara a gidanshi dake garin Kaduna.
Kungiyar ta kai ziyarar ne karkashin jagorancin lauya mai zaman kanshi Solomon Dalong da nufin kara karfafa dankon zumunci tsakanin Kirista da Musulmi da kuma yarda da juna.
Da yake hira da manema labarai yayin ziyarar, Solomon Dalong ya bayyana cewa, bude baki da ake yi tsakanin mabiya addinan biyu a garuruwa dabam dabam na kasar alama ce cewa, an fara samun zaman lafiya, ya kuma yi kira da a ci gaba da daukar matakan cudanya da fahimtar juna.
Kungiyar ta kai ziyarar ne karkashin jagorancin lauya mai zaman kanshi Solomon Dalong da nufin kara karfafa dankon zumunci tsakanin Kirista da Musulmi da kuma yarda da juna.
Da yake hira da manema labarai yayin ziyarar, Solomon Dalong ya bayyana cewa, bude baki da ake yi tsakanin mabiya addinan biyu a garuruwa dabam dabam na kasar alama ce cewa, an fara samun zaman lafiya, ya kuma yi kira da a ci gaba da daukar matakan cudanya da fahimtar juna.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.