Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Binciken Tashin Gobarar Gidan Yari a Kamaru


Hukumomi a Kamaru sun fara binciken wutar da ta tashi a babban gidan Yarin dake Doula mai tashar jirgin ruwa da tayi sanadiyar kwantar da wasu fursinoni uku a asibiti da munanan raunukan kunar wuta.

Wani jami’in kashe gobara yace wasu ma’aikatan kwana kwana biyu sun ji rauni a jiya Alhamis yayin da suke kokarin wutar da ta tashi a gidan yarin News Bell a birnin hada hadar.

Ma’aikatan kashe gobara sun hana wutar yaduwa zuwa wasu gine gine a unguwar mai yawan jama’a dake kusa da gidan Yarin.

Sai dai ba a gano musabbanin tashin gobarar ba ko kuma tashin wutar na da alaka da yawan cunkoson jama’a a gidan Yarin.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama ciki har da Amnesty International, sun ce cunkoson jama’a da rashin tsafta da rikici sune kalubalen da suka addabi gidajen Yarin Kamaru.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG