Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AMSOSHIN TAMBAYOYINKU: *Tarihin Cibiyoyin Tarihi Na Timbuktu *Musabbabin Yawan Faduwar Darajar Naira II


Ibrahim K Garba
Ibrahim K Garba

Masu sauraronmu assalamu alaikum; barkanmu dasake saduwa a wannan shirin na Amsoshin Tambayoyinku.

TAMBAYA 1:

“Don Allah VOA Hausa, ku tambaya min masana dan takaitaccen tarihin gidajen tarihi da kuma wuraren tarihi na Timbuktu da ke kasar Mali, wanda hukumar UNESCO ta ayyana a matsayin muhimman wuraren tarihi na duniya.

MAI TAMBAYA: Yusuf Abubakar, Bauchi, Najeriya

TAMBAYA 2:

Sai kuma kashi na biyu na amsar tambayar nan mai cewa “Salamu alaikum VOA Hausa. Don Allah ku tambaya min masana, ko me ke janyo faduwar darajar Naira a Najeriya? Shin ko me ya sa har yanzu darajar Nairar ta ke farfadowa. Shin laifin Gwamnati ne ko na yan kasuwa.”

MAI TAMBAYA: Idan an tuna, shi ne, Garba Nahali Kamba, Kebbin Najeriya.

AMSOSHI

Mun fara da amsar tambaya kan tarihin wuraren tarihi na Timbuktu da ke Mali. Masanin kayan tarihi da yadda ake adana su, da ke da zama a Abujan Najeriya, Malam Balan Karo, ya yi bayani.

Sai kuma kashi na biyu kuma na karshe na amsar tambaya kan musabbabin yawan faduwar darajar Naira a Najeriya. Idan an tuna, wakilinmu a shiyyar Adamawa/Taraba a Najeriya, Muhd Salisu Lado, ya samo amsa daga Dr Ahmed Tukur Umar na Jami’ar Modibbo Adama da ke Yola, Adamawa Najeriya, wanda ya karasa bayaninsa:

A sha bayani lafiya:

08-19-23 AMSOSHIN TAMBAYOYINKU - edited.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:12:13 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG