Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AMSOSHIN TAMBAYOYINKU: *Me Ya Sa Buga Kudi Ke Da Matukar Tsada A Najeriya? *Wadanne Harsuna Su Ka Fi Tasiri A Afurka?


Ibrahim K Garba
Ibrahim K Garba

Yau filin ya zo da amsoshi kan muhimman tambayoyi kamar yadda aka yi buga kudi ke da tsada a Najeriya da kuma harsuna mafiya tasiri a Afurka.

TAMBAYA 1:

Assalamma alaikum, bayan gaisuwa da fatan alkhairi, ga masu gabatar da wannan shirin, ga tambaya da na ke so ku amsa ma ni:

Gameda canjin launin kudi da za ayi a Nigeria, kamar yanda na gani a wasu kafofin yada labarai, ance za a Kashe har N58.21billion wajen buga sababin kudi N2.52billion.To wai idan haka gaskiya ne, me wan nan yake nufi ? Anci riba ko faduwa akayi kenan?

Wassalam Ku huta lafiya.

MAI TAMBAYAR: Dalhatu Manjos Gobir, Samaru Busstop Zaria, Jahar kaduna

TAMBAYA 2:

Assalamma alaikum voa Hausa. Don Allah a kasashenmu na afirka harsuna manya
manya, wadanda muke magana da su, kuma mutane su fahimta, guda nawa ne.

MASU TAMBAYA: Kawu Mairuwa Bajoga, da Alhaji Kari Bage Bajoga.

AMSA 1:

To bari mu fara da tambaya kan batun canjin kudi, idan mai tambaya, Dalhatu Manjos Gobir na tare da mu, ga amsarka da wakilin Sashin Hausa a yankin Adamawa, Muhammad Salisu Garba, ya samo daga Dr Adamu Babikwai malami a kwalejin horas da malamai mallakar gwamnatin Nigeria dake jihar Adamawa wato FCE yola, wanda ya ba da amsa kamar yadda za a ji.

AMSA 2:

Sai kuma maimaicin amsar tambaya kan manyan harsunan da ake amfani da su a Afurka sosai. Idan masu tambayar Kawu Mairuwa Bajoga da alh. Kari Bage na tare da mu, ga amsarku da wakilinmu a Adamawa, Muhammad Salisu Lado ya samo daga Dr. Mahdi Abba, Malami a jami’ar modibbo adama dake yola, jihar Adamawa, Najeriya, wanda ya yi bayani kamar yadda za a ji.

A yi saurare lafiya:

11-12-22 AMSOSHIN TAMBAYOYINKU.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:14:10 0:00

XS
SM
MD
LG