Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al'amura Sun Fara Daidaita A Jihar Filato


Jos, Nigeria
Jos, Nigeria

Jama'a sun bude wuraren kasuwancinsu gami da cigaba da harkokinsu kamar kullum.

Al’amura sun fara daidaituwa bayan rikicin da ya nemi kunno kai a Jihar Filato, bayan kashe wasu mutane 15 yan bindiga sukayi a Rukuba Road dake cikin garin Jos.

Duk da kone konen ababen hawa da ofishin Yan sanda da wasu matasa sukayi a jiya, a yau Jama’a sun bude wuraren kasuwancinsu gami da gudanar da harkokin su kamar kullum.

Jami’an tsaro a Jihar sun ce sun shawo kan lamarin. Ga Zainab Babaji dauke da cikakken rahoton.

Cigaban Zaman Lafiya A Jihar Filato
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:01 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG