Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Adadin Wadanda Suka Mutu A Ambaliyar Ruwa A Nijar Ya Haura 55


Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya mamaye kasar Nijer da ke Yammacin Afirka tun daga watan Yuni ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 55 sannan mutane 53,000 suka rasa matsugunansu, bisa ga cewar hukumomi.

Fiye da gidaje 4,800 ne ambaliyar ruwa ko zaftarewar kasa ta lalata, kuma an yi asarar shanu kusan 900, in ji Kanal Bako Boubacar, shugaban hukumar kare fararen hula a gidan rediyon gwamnati.

Yankunan da abin ya fi kamari su ne Maradi a kudu maso gabas, Agadez a hamadar arewa da Yamai babban birnin kasar, inda 16 suka mutu.

Jamhuriyar Nijar, matalauciyar kasa ce mara ruwa a yankin Sahel, da ke fama da matsanancin ambaliyar ruwa. Lokacin damina bashi da tsawo, kuma yawanci yana gudana ne daga Yuni zuwa Agusta ko Satumba, kodayake a cikin 'yan shekarun nan yayi ƙarfi sosai.

A shekarar da ta gabata, ambaliyar ruwa ta yi sanadiyyar asarar rayuka 73 abinda ya haddasa rikicin jinkai inda mutane miliyan 2.2 ke bukatar taimako, a cewar Majalisar Dinkin Duniya. A 2019, 57 sun mutu.

Adadin wadanda suka mutu daga daminar bana, wanda aka bayar a ranar 31 ga watan Yuli, ya kai 35 sannan mutane 26,532 sun rasa matsuguninsu.

XS
SM
MD
LG