Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Shirye Muke Mu Fafata Da Kwaddebuwa, Inji Shugaban Kwallon Kafa Ta Najeriya


Dan wasan Najeriya, Victor Osimhen a karawar Najeriya da Equatorial Guinea
Dan wasan Najeriya, Victor Osimhen a karawar Najeriya da Equatorial Guinea

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nigeria Alh. Ibrahim Gusau yace bashi da wani shakku akan wasan da Super Eagle zata kara da mai masaukin baki a gasar cin kofin Afrika da a ke yi yanzu haka a kasar Kwaddebuwa.

A wata zantawa da Muyar Amurka, Alhaji Ibrahim Gusau yace sun yi duk wani shirin da ya kamata domin tunkarar wannan wasa da za a gudanar a ranar 18 ga watan Jana'irun 2024 cikin ikon Allah.

A dangane da wasan da Nigeria ta Buga a baya Alh. Gusau yace suna baiwa 'yan Nigeriar hakuri akan abinda ya faru kuma a yanzu sun dauki mataki kuma hakan ba za ta sake faruwa ba.

Ya kara da cewa suna da kwarin guiwa sosai akan 'yan wasan Nigeria.

Haka zalika, Alh. Gusau yace ba su da wata matsala akan biyan hakkokin 'yan wasan na Super Eagles domin Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da duk wani abu da aka rubuta domin biyan 'yan wasan,

Sai dai ya bukaci 'yan Najeriar su cigaba da yi masu addu'o'i na musamman domin ganin sun dawo da wannan Kofi.

Ga cikakken hirarsa a sauti da wakilin Muryar Amurka, Mustapha Nasiru Batsari.

A Shirye Muke Mu Fafata Da Kwaddebuwa, Inji Shugaban Kwallon Kafa Ta Najeriya
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:16 0:00

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG