Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A BARI YA HUCE: Karrama Marigayi Ibrahim Abdul'aziz, Fabrairu 06, 2021


Ibrahim Abdul'aziz
Ibrahim Abdul'aziz

Ibrahim Abdul'ziz wanda kafin rasuwarsa ya ke dauko wa Sashen Hausa rahotanni daga jihohin Adamawa da Taraba, ya gamu da ajalinsa ne a kan hanyar shi zuwa Bauchi domin halartar daurin auren abokinsa.

Abdul'aziz yana daya daga cikin hazikan wakilan Sashen Hausa wanda banda rahotanni da yake daukowa, loto-loto ya kan jagoranci gabatar da shirye shirye na musamman a Sashen Hausa. Ya kuma nuna kwarewa wajen dauko rahotannin da suka shafi rayuwar talaka ta yau da kullum, da zamantakewar al'umma ,da kuma harkokin siyasa.

Saurari wannan shirin na musamman da aka shirya domin karrama marigayin:

A BARI YA HUCE: Tunawa da rayuwar Ibrahim Abdul'aziz-24:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:23:45 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG