Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka da Wasu Kasashen Turai Sun Kakabawa Wasu Jami'an Jamhuriyar Dimokradiyar Kwango Takunkumi


Screenshot from a Parliament broadcast of New Zealand Speaker Trevor Mallard feeding a Member of Parliament’s baby during a parliamentary session in Wellington, Aug. 21, 2019. (New Zealand Parliament and Speaker's Office/Handout)
Screenshot from a Parliament broadcast of New Zealand Speaker Trevor Mallard feeding a Member of Parliament’s baby during a parliamentary session in Wellington, Aug. 21, 2019. (New Zealand Parliament and Speaker's Office/Handout)

Amurka da wasu kasashen Turai sun kargafawa wasu jami’an gwamnatin Junhuriyar Demokradiyar Congo takunkumin horo saboda rawar da suka taka wajen tada zaune-tsaye don a jinkirta gudanarda zabe a kasar.

Kamata yayi wa’adin mulki na biyu kuma na karshe na shugaba Joseph Kabila ya kare nan da mako guda, a ran 19 ga watan nan na Disamba, amma zai ci gaba da zamansa akan karaga a dalilin wata yarjejeiyar da akace an kulla da wani rukuni na ‘yan adawa, wanda zai bashi damar zama a kan kujerarsa ta mulki har zuwa shekarar 2018.

Sai dai mafi yawan jam’iyyun adawa duk sun ki yarda da wannan shirin, suna cewa sai shugaban ya sauka daga mulki a ranar Litinin mai zuwa.

Daga cikin wadanda aka dauki matakan horaswa a kansu din har da mataimakin frayim-ministan Congo din, Evariste Boshab da kuma Kalev Mutondo, shugaban Hukumar Leken Asiri ta kasar.

XS
SM
MD
LG